Hausa - Sorah Al-Balad ( The City )

Noble Quran » Hausa » Sorah Al-Balad ( The City )

Choose the reader


Hausa

Sorah Al-Balad ( The City ) - Verses Number 20
لَا أُقْسِمُ بِهَٰذَا الْبَلَدِ ( 1 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 1
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.
وَأَنتَ حِلٌّ بِهَٰذَا الْبَلَدِ ( 2 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 2
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.
وَوَالِدٍ وَمَا وَلَدَ ( 3 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 3
Da mahaifi da abin da ya haifa.
لَقَدْ خَلَقْنَا الْإِنسَانَ فِي كَبَدٍ ( 4 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 4
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.
أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌ ( 5 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 5
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?
يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًا لُّبَدًا ( 6 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 6
Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"
أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُ أَحَدٌ ( 7 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 7
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?
أَلَمْ نَجْعَل لَّهُ عَيْنَيْنِ ( 8 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 8
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?
وَلِسَانًا وَشَفَتَيْنِ ( 9 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 9
Da harshe, da leɓɓa biyu.
وَهَدَيْنَاهُ النَّجْدَيْنِ ( 10 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 10
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?
فَلَا اقْتَحَمَ الْعَقَبَةَ ( 11 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 11
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْعَقَبَةُ ( 12 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 12
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
فَكُّ رَقَبَةٍ ( 13 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 13
Ita ce fansar wuyan bãwa.
أَوْ إِطْعَامٌ فِي يَوْمٍ ذِي مَسْغَبَةٍ ( 14 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 14
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.
يَتِيمًا ذَا مَقْرَبَةٍ ( 15 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 15
Ga marãya ma'abũcin zumunta.
أَوْ مِسْكِينًا ذَا مَتْرَبَةٍ ( 16 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 16
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.
ثُمَّ كَانَ مِنَ الَّذِينَ آمَنُوا وَتَوَاصَوْا بِالصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا بِالْمَرْحَمَةِ ( 17 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 17
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
أُولَٰئِكَ أَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِ ( 18 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 18
Waɗannan ne ma'abũta albarka
وَالَّذِينَ كَفَرُوا بِآيَاتِنَا هُمْ أَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِ ( 19 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 19
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci
عَلَيْهِمْ نَارٌ مُّؤْصَدَةٌ ( 20 ) Al-Balad ( The City ) - Ayaa 20
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.

Random Books

Choose language

Choose Sorah

Random Books

Choose tafseer

Participate

Bookmark and Share