Hausa - Sorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder)

Noble Quran » Hausa » Sorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder)

Choose the reader


Hausa

Sorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Verses Number 25
إِذَا السَّمَاءُ انشَقَّتْ ( 1 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 1
Idan sama ta kẽce,
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ ( 2 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 2
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
وَإِذَا الْأَرْضُ مُدَّتْ ( 3 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 3
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ ( 4 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 4
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ ( 5 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 5
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَاقِيهِ ( 6 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 6
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ ( 7 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 7
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا ( 8 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 8
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
وَيَنقَلِبُ إِلَىٰ أَهْلِهِ مَسْرُورًا ( 9 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 9
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ وَرَاءَ ظَهْرِهِ ( 10 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 10
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
فَسَوْفَ يَدْعُو ثُبُورًا ( 11 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 11
To, zã shi dinga kiran halaka!
وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا ( 12 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 12
Kuma ya shiga sa'ĩr.
إِنَّهُ كَانَ فِي أَهْلِهِ مَسْرُورًا ( 13 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 13
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
إِنَّهُ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ ( 14 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 14
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
بَلَىٰ إِنَّ رَبَّهُ كَانَ بِهِ بَصِيرًا ( 15 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 15
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
فَلَا أُقْسِمُ بِالشَّفَقِ ( 16 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 16
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
وَاللَّيْلِ وَمَا وَسَقَ ( 17 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 17
Da dare, da abin da ya ƙunsa.
وَالْقَمَرِ إِذَا اتَّسَقَ ( 18 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 18
Da watã idan (haskensa) ya cika.
لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍ ( 19 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 19
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ ( 20 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 20
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ الْقُرْآنُ لَا يَسْجُدُونَ ۩ ( 21 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 21
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?
بَلِ الَّذِينَ كَفَرُوا يُكَذِّبُونَ ( 22 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 22
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
وَاللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ ( 23 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 23
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ ( 24 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 24
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍ ( 25 ) Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) - Ayaa 25
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.

Random Books

Choose language

Choose Sorah

Random Books

Choose tafseer

Participate

Bookmark and Share