Hausa - Sorah Al-Qalam ( The Pen )

Noble Quran » Hausa » Sorah Al-Qalam ( The Pen )

Choose the reader


Hausa

Sorah Al-Qalam ( The Pen ) - Verses Number 52
ن ۚ وَالْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَ ( 1 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 1
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
مَا أَنتَ بِنِعْمَةِ رَبِّكَ بِمَجْنُونٍ ( 2 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 2
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
وَإِنَّ لَكَ لَأَجْرًا غَيْرَ مَمْنُونٍ ( 3 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 3
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍ ( 4 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 4
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
فَسَتُبْصِرُ وَيُبْصِرُونَ ( 5 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 5
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
بِأَييِّكُمُ الْمَفْتُونُ ( 6 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 6
Ga wanenku haukã take.
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِ وَهُوَ أَعْلَمُ بِالْمُهْتَدِينَ ( 7 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 7
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
فَلَا تُطِعِ الْمُكَذِّبِينَ ( 8 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 8
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
وَدُّوا لَوْ تُدْهِنُ فَيُدْهِنُونَ ( 9 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 9
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
وَلَا تُطِعْ كُلَّ حَلَّافٍ مَّهِينٍ ( 10 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 10
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
هَمَّازٍ مَّشَّاءٍ بِنَمِيمٍ ( 11 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 11
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
مَّنَّاعٍ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ ( 12 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 12
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
عُتُلٍّ بَعْدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ ( 13 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 13
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
أَن كَانَ ذَا مَالٍ وَبَنِينَ ( 14 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 14
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ آيَاتُنَا قَالَ أَسَاطِيرُ الْأَوَّلِينَ ( 15 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 15
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
سَنَسِمُهُ عَلَى الْخُرْطُومِ ( 16 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 16
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
إِنَّا بَلَوْنَاهُمْ كَمَا بَلَوْنَا أَصْحَابَ الْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ ( 17 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 17
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
وَلَا يَسْتَثْنُونَ ( 18 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 18
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
فَطَافَ عَلَيْهَا طَائِفٌ مِّن رَّبِّكَ وَهُمْ نَائِمُونَ ( 19 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 19
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
فَأَصْبَحَتْ كَالصَّرِيمِ ( 20 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 20
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
فَتَنَادَوْا مُصْبِحِينَ ( 21 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 21
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
أَنِ اغْدُوا عَلَىٰ حَرْثِكُمْ إِن كُنتُمْ صَارِمِينَ ( 22 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 22
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
فَانطَلَقُوا وَهُمْ يَتَخَافَتُونَ ( 23 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 23
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
أَن لَّا يَدْخُلَنَّهَا الْيَوْمَ عَلَيْكُم مِّسْكِينٌ ( 24 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 24
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
وَغَدَوْا عَلَىٰ حَرْدٍ قَادِرِينَ ( 25 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 25
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوا إِنَّا لَضَالُّونَ ( 26 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 26
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ ( 27 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 27
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُل لَّكُمْ لَوْلَا تُسَبِّحُونَ ( 28 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 28
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
قَالُوا سُبْحَانَ رَبِّنَا إِنَّا كُنَّا ظَالِمِينَ ( 29 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 29
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَلَاوَمُونَ ( 30 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 30
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
قَالُوا يَا وَيْلَنَا إِنَّا كُنَّا طَاغِينَ ( 31 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 31
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
عَسَىٰ رَبُّنَا أَن يُبْدِلَنَا خَيْرًا مِّنْهَا إِنَّا إِلَىٰ رَبِّنَا رَاغِبُونَ ( 32 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 32
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
كَذَٰلِكَ الْعَذَابُ ۖ وَلَعَذَابُ الْآخِرَةِ أَكْبَرُ ۚ لَوْ كَانُوا يَعْلَمُونَ ( 33 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 33
Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّاتِ النَّعِيمِ ( 34 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 34
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
أَفَنَجْعَلُ الْمُسْلِمِينَ كَالْمُجْرِمِينَ ( 35 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 35
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ ( 36 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 36
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
أَمْ لَكُمْ كِتَابٌ فِيهِ تَدْرُسُونَ ( 37 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 37
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
إِنَّ لَكُمْ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ ( 38 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 38
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
أَمْ لَكُمْ أَيْمَانٌ عَلَيْنَا بَالِغَةٌ إِلَىٰ يَوْمِ الْقِيَامَةِ ۙ إِنَّ لَكُمْ لَمَا تَحْكُمُونَ ( 39 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 39
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
سَلْهُمْ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ ( 40 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 40
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
أَمْ لَهُمْ شُرَكَاءُ فَلْيَأْتُوا بِشُرَكَائِهِمْ إِن كَانُوا صَادِقِينَ ( 41 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 41
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
يَوْمَ يُكْشَفُ عَن سَاقٍ وَيُدْعَوْنَ إِلَى السُّجُودِ فَلَا يَسْتَطِيعُونَ ( 42 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 42
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.
خَاشِعَةً أَبْصَارُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۖ وَقَدْ كَانُوا يُدْعَوْنَ إِلَى السُّجُودِ وَهُمْ سَالِمُونَ ( 43 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 43
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
فَذَرْنِي وَمَن يُكَذِّبُ بِهَٰذَا الْحَدِيثِ ۖ سَنَسْتَدْرِجُهُم مِّنْ حَيْثُ لَا يَعْلَمُونَ ( 44 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 44
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
وَأُمْلِي لَهُمْ ۚ إِنَّ كَيْدِي مَتِينٌ ( 45 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 45
Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.
أَمْ تَسْأَلُهُمْ أَجْرًا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍ مُّثْقَلُونَ ( 46 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 46
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
أَمْ عِندَهُمُ الْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ ( 47 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 47
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
فَاصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ الْحُوتِ إِذْ نَادَىٰ وَهُوَ مَكْظُومٌ ( 48 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 48
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
لَّوْلَا أَن تَدَارَكَهُ نِعْمَةٌ مِّن رَّبِّهِ لَنُبِذَ بِالْعَرَاءِ وَهُوَ مَذْمُومٌ ( 49 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 49
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
فَاجْتَبَاهُ رَبُّهُ فَجَعَلَهُ مِنَ الصَّالِحِينَ ( 50 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 50
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
وَإِن يَكَادُ الَّذِينَ كَفَرُوا لَيُزْلِقُونَكَ بِأَبْصَارِهِمْ لَمَّا سَمِعُوا الذِّكْرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُ لَمَجْنُونٌ ( 51 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 51
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَ ( 52 ) Al-Qalam ( The Pen ) - Ayaa 52
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.

Random Books

Choose language

Choose Sorah

Random Books

Choose tafseer

Participate

Bookmark and Share