Noble Quran » Hausa » Sorah Al-Mutaffifin (Those Who Deal in Fraud)
Choose the reader
Hausa
Sorah Al-Mutaffifin (Those Who Deal in Fraud) - Verses Number 36
الَّذِينَ إِذَا اكْتَالُوا عَلَى النَّاسِ يَسْتَوْفُونَ ( 2 )

Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu.
وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ ( 3 )

Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikẽli, suna ragẽwa
أَلَا يَظُنُّ أُولَٰئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ ( 4 )

Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba?
يَوْمَ يَقُومُ النَّاسُ لِرَبِّ الْعَالَمِينَ ( 6 )

Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta?
كَلَّا إِنَّ كِتَابَ الْفُجَّارِ لَفِي سِجِّينٍ ( 7 )

Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn.
وَمَا يُكَذِّبُ بِهِ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ ( 12 )

Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi.
إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ آيَاتُنَا قَالَ أَسَاطِيرُ الْأَوَّلِينَ ( 13 )

Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne.
كَلَّا ۖ بَلْ ۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا يَكْسِبُونَ ( 14 )

A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu.
كَلَّا إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّمَحْجُوبُونَ ( 15 )

A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne.
ثُمَّ يُقَالُ هَٰذَا الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ ( 17 )

Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi."
كَلَّا إِنَّ كِتَابَ الْأَبْرَارِ لَفِي عِلِّيِّينَ ( 18 )

A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna?
تَعْرِفُ فِي وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ النَّعِيمِ ( 24 )

Kana sani a cikin huskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima.
يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍ مَّخْتُومٍ ( 25 )

Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta.
خِتَامُهُ مِسْكٌ ۚ وَفِي ذَٰلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ الْمُتَنَافِسُونَ ( 26 )

¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma.
عَيْنًا يَشْرَبُ بِهَا الْمُقَرَّبُونَ ( 28 )

(Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi.
إِنَّ الَّذِينَ أَجْرَمُوا كَانُوا مِنَ الَّذِينَ آمَنُوا يَضْحَكُونَ ( 29 )

Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya.
وَإِذَا انقَلَبُوا إِلَىٰ أَهْلِهِمُ انقَلَبُوا فَكِهِينَ ( 31 )

Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci.
وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوا إِنَّ هَٰؤُلَاءِ لَضَالُّونَ ( 32 )

Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne."
وَمَا أُرْسِلُوا عَلَيْهِمْ حَافِظِينَ ( 33 )

Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu.
Random Books
- SAKO ZUWA GA ALHAZAI DA 'YAN UMRA-
Source : http://www.islamhouse.com/p/156358
- Matsayin Mata A Musulunci, Yahudanci da Nasaranci-
Source : http://www.islamhouse.com/p/191549
- SIFAR HAJJI DA UMRA-
Source : http://www.islamhouse.com/p/315025
- TAFARKIN SUNNAHTAFARKIN SUNNAH tattaunawa ta ruwan sanyi tsakanin ibnu taimiyyah da ‘yan shi’ar zamaninsa
Source : http://www.islamhouse.com/p/172222
- INA ALLAH YA KE?INA ALLAH YA KE? (Nazari Akan Daukakar Allah Bisa Al’arshi A Ra’ayin Magabata Da Na Bayansu)
Source : http://www.islamhouse.com/p/259886