Hausa - Sorah At-Tur ( The Mount )

Noble Quran » Hausa » Sorah At-Tur ( The Mount )

Choose the reader


Hausa

Sorah At-Tur ( The Mount ) - Verses Number 49
وَالطُّورِ ( 1 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 1
Inã rantsuwa da ¦ũr (Dũtsen Mũsã).
وَكِتَابٍ مَّسْطُورٍ ( 2 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 2
Da wani littãfi rubũtacce.
فِي رَقٍّ مَّنشُورٍ ( 3 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 3
A cikin wata takardar fãta shimfiɗaɗɗa.
وَالْبَيْتِ الْمَعْمُورِ ( 4 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 4
Da Gidan da aka rãyar da shi (da ibãda).
وَالسَّقْفِ الْمَرْفُوعِ ( 5 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 5
Da rufin nan da aka ɗaukaka.
وَالْبَحْرِ الْمَسْجُورِ ( 6 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 6
Da tẽkun nan da aka cika (da ruwa).
إِنَّ عَذَابَ رَبِّكَ لَوَاقِعٌ ( 7 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 7
Lalle, azãbar Ubangijinka, haƙĩƙa, mai aukuwa ce.
مَّا لَهُ مِن دَافِعٍ ( 8 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 8
Bã ta da mai tunkuɗẽwa.
يَوْمَ تَمُورُ السَّمَاءُ مَوْرًا ( 9 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 9
Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.
وَتَسِيرُ الْجِبَالُ سَيْرًا ( 10 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 10
Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.
فَوَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ ( 11 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 11
To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.
الَّذِينَ هُمْ فِي خَوْضٍ يَلْعَبُونَ ( 12 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 12
Waɗanda suke a cikin kududdufi sunã wãsã.
يَوْمَ يُدَعُّونَ إِلَىٰ نَارِ جَهَنَّمَ دَعًّا ( 13 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 13
Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.
هَٰذِهِ النَّارُ الَّتِي كُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ ( 14 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 14
(A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."
أَفَسِحْرٌ هَٰذَا أَمْ أَنتُمْ لَا تُبْصِرُونَ ( 15 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 15
"To, shin wannan sihiri ne kõ kuwa kũ ne bã ku gani?"
اصْلَوْهَا فَاصْبِرُوا أَوْ لَا تَصْبِرُوا سَوَاءٌ عَلَيْكُمْ ۖ إِنَّمَا تُجْزَوْنَ مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ ( 16 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 16
"Ku shigẽ ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai anã yi muku sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَنَعِيمٍ ( 17 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 17
Lalle, mãsu taƙawa, sunã a cikin gidãjen Aljanna da wata ni'ima.
فَاكِهِينَ بِمَا آتَاهُمْ رَبُّهُمْ وَوَقَاهُمْ رَبُّهُمْ عَذَابَ الْجَحِيمِ ( 18 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 18
Sunã mãsu jin dãɗi da abin da Ubangijinsu Ya ba su, kuma Ubangijinsu Ya tsãre musu azãbar Jahĩm.
كُلُوا وَاشْرَبُوا هَنِيئًا بِمَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ ( 19 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 19
(A ce musu): "Ku ci, ku sha, da ni'ima, dõmin abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ سُرُرٍ مَّصْفُوفَةٍ ۖ وَزَوَّجْنَاهُم بِحُورٍ عِينٍ ( 20 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 20
Sunã kishingiɗe a kan karagu waɗanda ke cikin sahu, kuma Muka aurar da su waɗansu mãtã mãsu farin idãnu, mãsu girmansu.
وَالَّذِينَ آمَنُوا وَاتَّبَعَتْهُمْ ذُرِّيَّتُهُم بِإِيمَانٍ أَلْحَقْنَا بِهِمْ ذُرِّيَّتَهُمْ وَمَا أَلَتْنَاهُم مِّنْ عَمَلِهِم مِّن شَيْءٍ ۚ كُلُّ امْرِئٍ بِمَا كَسَبَ رَهِينٌ ( 21 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 21
Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma zũriyarsu suka bĩ su ga ĩmãnin, Mun riskar da zũriyarsu da su, alhãli kuwa bã da Mun rage musu kõme ba daga aikinsu, kõwane mutum jingina ne ga abin da ya sana'anta.
وَأَمْدَدْنَاهُم بِفَاكِهَةٍ وَلَحْمٍ مِّمَّا يَشْتَهُونَ ( 22 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 22
Kuma Muka yalwata musu 'ya'yan itãce da nãma irin wanda suke marmari.
يَتَنَازَعُونَ فِيهَا كَأْسًا لَّا لَغْوٌ فِيهَا وَلَا تَأْثِيمٌ ( 23 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 23
Sunã mĩƙa wa jũnansu a cikinta hinjãlan giya, wadda bãbu yãsassar magana a cikinta, kuma bãbu jin nauyin zunubi.
وَيَطُوفُ عَلَيْهِمْ غِلْمَانٌ لَّهُمْ كَأَنَّهُمْ لُؤْلُؤٌ مَّكْنُونٌ ( 24 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 24
Kuma waɗansu samãri nã gẽwayãwa a kansu, kamar dai sũ lu'ulu'u ne wanda ke kulle.
وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ ( 25 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 25
Waɗansunsu suka fuskanta zuwa ga waɗansu, sunã tambayar jũna.
قَالُوا إِنَّا كُنَّا قَبْلُ فِي أَهْلِنَا مُشْفِقِينَ ( 26 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 26
Suka ce: "Lalle mũ mun kasance a gabãnin wannan (a dũniya) a cikin iyãlanmu munã jin tsõro."
فَمَنَّ اللَّهُ عَلَيْنَا وَوَقَانَا عَذَابَ السَّمُومِ ( 27 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 27
"To, Allah Yã yi mana kyautar falala, kuma Yã tsare mana azãbar iskar zãfi."
إِنَّا كُنَّا مِن قَبْلُ نَدْعُوهُ ۖ إِنَّهُ هُوَ الْبَرُّ الرَّحِيمُ ( 28 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 28
"Lalle mũ mun kasance, a gãbanin haka, munã kiran sa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai kyautatãwa, Mai rahama."
فَذَكِّرْ فَمَا أَنتَ بِنِعْمَتِ رَبِّكَ بِكَاهِنٍ وَلَا مَجْنُونٍ ( 29 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 29
To, ka tunãtar kai fa sabõda ni'imar Ubangjinka, bã bõka kake ba, kuma bã mahaukaci ba.
أَمْ يَقُولُونَ شَاعِرٌ نَّتَرَبَّصُ بِهِ رَيْبَ الْمَنُونِ ( 30 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 30
Shin zã su ce: "Mawãƙi ne, munã jiran, masĩfun mutuwa game da shĩ"?
قُلْ تَرَبَّصُوا فَإِنِّي مَعَكُم مِّنَ الْمُتَرَبِّصِينَ ( 31 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 31
Ka ce: "Ku yi jira, domin nĩ ma lalle inã a cikin mãsu jira tãre da ku."
أَمْ تَأْمُرُهُمْ أَحْلَامُهُم بِهَٰذَا ۚ أَمْ هُمْ قَوْمٌ طَاغُونَ ( 32 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 32
Shin, hankulansu ne ke umarin su da wannan, kõ kuwa sũ wasu mutãne ne mãsu ƙetare haddi?
أَمْ يَقُولُونَ تَقَوَّلَهُ ۚ بَل لَّا يُؤْمِنُونَ ( 33 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 33
Shin, cẽwa suke yi: "Shi ne ke ƙãga faɗarsa"? Ã'a ba su dai yi ĩmãni ba.
فَلْيَأْتُوا بِحَدِيثٍ مِّثْلِهِ إِن كَانُوا صَادِقِينَ ( 34 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 34
Sai su zõ da wani lãbãri mai misãlinsa idan sun kasance sũmãsu gaskiya ne.
أَمْ خُلِقُوا مِنْ غَيْرِ شَيْءٍ أَمْ هُمُ الْخَالِقُونَ ( 35 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 35
Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?
أَمْ خَلَقُوا السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ ۚ بَل لَّا يُوقِنُونَ ( 36 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 36
Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba.
أَمْ عِندَهُمْ خَزَائِنُ رَبِّكَ أَمْ هُمُ الْمُصَيْطِرُونَ ( 37 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 37
Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?
أَمْ لَهُمْ سُلَّمٌ يَسْتَمِعُونَ فِيهِ ۖ فَلْيَأْتِ مُسْتَمِعُهُم بِسُلْطَانٍ مُّبِينٍ ( 38 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 38
Shin, sunã da wani tsãni ne wanda suke (hawa sunã) saurãron (lãbãrin samã) a cikinsa? Sai mai saurarõnsu ya zo da wani dalĩli bayyananne.
أَمْ لَهُ الْبَنَاتُ وَلَكُمُ الْبَنُونَ ( 39 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 39
Shin, Yanã da 'ya'ya mãtã ne kuma kũ, kunã da ɗiya maza ne?
أَمْ تَسْأَلُهُمْ أَجْرًا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍ مُّثْقَلُونَ ( 40 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 40
Shin, kanã tambayar su wata ijãra ne, sabõda haka suka zama mãsu jin nauyin biyan tãrar?
أَمْ عِندَهُمُ الْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ ( 41 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 41
Shin, a wurinsu akwai ilmin gaibi, sabõda haka sunã rubũtãwa?
أَمْ يُرِيدُونَ كَيْدًا ۖ فَالَّذِينَ كَفَرُوا هُمُ الْمَكِيدُونَ ( 42 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 42
Shin, sunã nufin wani kaidi ne? To, waɗanda suka kãfirta sũ ne waɗanda ake yi wa kaidi.
أَمْ لَهُمْ إِلَٰهٌ غَيْرُ اللَّهِ ۚ سُبْحَانَ اللَّهِ عَمَّا يُشْرِكُونَ ( 43 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 43
Shin, sunã da wani abin bautãwa ne wanda bã Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke yi na shirki!
وَإِن يَرَوْا كِسْفًا مِّنَ السَّمَاءِ سَاقِطًا يَقُولُوا سَحَابٌ مَّرْكُومٌ ( 44 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 44
Kuma idan sun ga wani ɓaɓɓake daga samã yãnã fãɗuwa, sai su ce wani girgije ne, mai hauhawar jũna.
فَذَرْهُمْ حَتَّىٰ يُلَاقُوا يَوْمَهُمُ الَّذِي فِيهِ يُصْعَقُونَ ( 45 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 45
To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sũmar da su a cikinsa.
يَوْمَ لَا يُغْنِي عَنْهُمْ كَيْدُهُمْ شَيْئًا وَلَا هُمْ يُنصَرُونَ ( 46 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 46
Rãnar da kaidinsu bã ya wadãtar masu da kõme, kuma bã a taimakon su.
وَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا عَذَابًا دُونَ ذَٰلِكَ وَلَٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ ( 47 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 47
Kuma lalle, waɗannan da suka yi zãluncin, sunã da azãba (a nan dũniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba.
وَاصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ فَإِنَّكَ بِأَعْيُنِنَا ۖ وَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ حِينَ تَقُومُ ( 48 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 48
Sai ka yi hakuri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kanã idãnunMu, kuma ka tsarkake Ubangijinka da (tasbĩhi) game da gõde Masa a lõkacin da kake tãshi tsaye (dõmin salla kõ wani abu).
وَمِنَ اللَّيْلِ فَسَبِّحْهُ وَإِدْبَارَ النُّجُومِ ( 49 ) At-Tur ( The Mount ) - Ayaa 49
Kuma daga dare, sai ka tsarkake Shi (da tasbĩhin) dalõkacin jũyãwar taurãri.

Random Books

Choose language

Choose Sorah

Random Books

Choose tafseer

Participate

Bookmark and Share