Hausa - Sorah Al-Fajr ( The Dawn )

Noble Quran » Hausa » Sorah Al-Fajr ( The Dawn )

Choose the reader


Hausa

Sorah Al-Fajr ( The Dawn ) - Verses Number 30
وَالْفَجْرِ ( 1 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 1
Inã rantsuwa da alfijiri.
وَلَيَالٍ عَشْرٍ ( 2 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 2
Da darũruwa gõma.
وَالشَّفْعِ وَالْوَتْرِ ( 3 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 3
Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.
وَاللَّيْلِ إِذَا يَسْرِ ( 4 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 4
Da dare idan yana shũɗewa.
هَلْ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٌ لِّذِي حِجْرٍ ( 5 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 5
Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?
أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ ( 6 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 6
Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?
إِرَمَ ذَاتِ الْعِمَادِ ( 7 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 7
Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.
الَّتِي لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِي الْبِلَادِ ( 8 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 8
Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).
وَثَمُودَ الَّذِينَ جَابُوا الصَّخْرَ بِالْوَادِ ( 9 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 9
Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?
وَفِرْعَوْنَ ذِي الْأَوْتَادِ ( 10 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 10
Da Fir'auna mai turãku.
الَّذِينَ طَغَوْا فِي الْبِلَادِ ( 11 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 11
Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?
فَأَكْثَرُوا فِيهَا الْفَسَادَ ( 12 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 12
Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.
فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ ( 13 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 13
Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.
إِنَّ رَبَّكَ لَبِالْمِرْصَادِ ( 14 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 14
Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.
فَأَمَّا الْإِنسَانُ إِذَا مَا ابْتَلَاهُ رَبُّهُ فَأَكْرَمَهُ وَنَعَّمَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَكْرَمَنِ ( 15 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 15
To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."
وَأَمَّا إِذَا مَا ابْتَلَاهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَهَانَنِ ( 16 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 16
Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."
كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ الْيَتِيمَ ( 17 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 17
A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!
وَلَا تَحَاضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ ( 18 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 18
Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!
وَتَأْكُلُونَ التُّرَاثَ أَكْلًا لَّمًّا ( 19 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 19
Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.
وَتُحِبُّونَ الْمَالَ حُبًّا جَمًّا ( 20 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 20
Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.
كَلَّا إِذَا دُكَّتِ الْأَرْضُ دَكًّا دَكًّا ( 21 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 21
A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.
وَجَاءَ رَبُّكَ وَالْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا ( 22 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 22
Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.
وَجِيءَ يَوْمَئِذٍ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ وَأَنَّىٰ لَهُ الذِّكْرَىٰ ( 23 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 23
Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!
يَقُولُ يَا لَيْتَنِي قَدَّمْتُ لِحَيَاتِي ( 24 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 24
Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُ أَحَدٌ ( 25 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 25
To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.
وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُ أَحَدٌ ( 26 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 26
Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.
يَا أَيَّتُهَا النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ ( 27 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 27
Yã kai rai mai natsuwa!
ارْجِعِي إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةً مَّرْضِيَّةً ( 28 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 28
Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).
فَادْخُلِي فِي عِبَادِي ( 29 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 29
Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).
وَادْخُلِي جَنَّتِي ( 30 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Ayaa 30
Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).

Random Books

Choose language

Choose Sorah

Random Books

Choose tafseer

Participate

Bookmark and Share